Bayan da aka kai harin ƙunar baƙin wake a ƙasar Faransa a ranar Juma’a 13/Nuwamba/2015 mutane da dama ba su ji daɗin yadda babban shafin sada zumuncin nan mai suna Facebook ya fito da wani tsari na canza hoton da ke wakiltar mutum zuwa tutar ƙasar Faransa.
Mutane daga kowane ɓangare na duniya sun nuna baƙin cikinsu dangane da wannan mummunan hari na ranar Juma’a sai dai a wani ɓangare kuma an samu ƙorafe-ƙorafen jama’a kasancewar kamfanin Facebook ya nema jama’ar duniya da su yi wa kasar faransar addu’o’in zaman lafiya.
Wannan kira da kuma neman jama’a su san hotunan su ya baƙanta wa mutane da dama rai musamman mutanen yankin Larabawa da kuma nahiyar Afirka, musamman saboda ganin irin zubar da jini da ake yi ba dare babu rana a yankunan amma kuma daidai da nuna wani abu yana faruwa wannan kamfani bai taɓa nunawa ba.
Hakan ya san wani shahararren marubuci mai kishin ƙasa Jafar Jafar ya rubuta zungureriyar wasiƙa zuwa ga Mark Zuckerberg wanda shi ne shugaban wannan kamfani yana mai nuna damuwarsa da ko in kula da bai nunawa ga jama’ar Afirka musamman idan aka dubi cewar mutane kusan sama da dubu goma sha takwas sun rasa rayukansu a hare-haren da ƙungiyar Boko Haram take kai wa a Arewacin Najeriya.
Ba ma Jafar da ya yi wannan rubutun ba kusan mutane sun yi amfani da wannan kiran da shi Mark Zuckerberg ya yi suna canza hotunan su zuwa hotunan ƙasarsu, kuma suka riƙa yin amfani da kalmar bai ɗaya (Harsh Tag) suna cewar ayi wa duniya baki ɗayanta addu’ar neman zaman lafiya.
SAFETY CHECK
Wannan shi ne tsarin da kamfanin facebook suka fito da shi a yau Labara 18/Nuwamba/2015 bayan da aka kai harin da ya hallaka mutane a ƙalla talatin a garin Adamawa.
Wannan tsari ne da yake bai wa duk wanda yake kusa da inda abin ya faru ya sanar da al’umma irin halin da yake ciki na yin mamakin cewar yana lafiya ko kuma shi babu abin da ya same shi.
Wannan ba ƙaramin ci gaba ba ne idan muka yi la’akari da irin ƙorafe-ƙorafen da jama’a suke yi na cewar ana nuna musu launin fata.
Duk da haka, wasu jama’a suna ganin cewar wannan fito da wannan tsari ba wani abin a zo a gani ba ne, domin har zuwa yanzu kamfanin bai dawo da tsarin da zai ba ka damar ka canza hotonka zuwa ga tutar Najeriya ba. A nasu ra’ayin, jama’a suna ganin idan dai ba nuna wariyar launin fata ba ya kamata a ce shi ma wancan tsarin na canza hoto yana aiki, kuma suna ganin kamar yadda ya yi magana a cikin shafinsa na a nema wa Faransa zaman lafiya, ba wai dawo da tsarin faɗin yanayin da mutum yake ciki za suyiba, magana zai yi.
Sai dai mu ce Allah Ya kyauta kuma ya gafarta wa waɗanda suka riga mu da imani amin.
Kodayake wanna shine lokaci na farko dana farajin wannan manana, Kuma nasan dama turawa basu dauki wani mutum da daraja indai ba nasuba, Amma menene wannan Abu yake nufi sannan ta fuskar kawo agaji ga wadanda abin yashafa ko kariya?