Gabatarwa
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Maɗaukakin Sarki, Mabuwayi mai Hikima, wanda ya sanar da mutum game da alkalami, ya sanar da mutum abin da bai sani ba, ya fitar da zamani mabanbanta da kuma shiryar da mutanen da suke cikin wannan zamani da hanyoyin da za su yi kira zuwa ga tafarkinsa.
Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabin Rahama wanda ya sanar da Sahabbansa cewar “Ku kuka fi sani ga al’amarin duniyar ku” tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da Iyalinsa da Sahabbansa da wanda suka bi shi da gaskiya har zuwa ranar tashin Alkiyama.
Social media a wannan zamani na daya daga cikin hanyoyin da jama’a suke yin amfani da su domin isar da sakwanni ko kuma karantawa da karantarwa, da ji ko gani na abubuwan da suka shafi rayuwar mu ta yau da kullum. Kuma bunƙasar amfani da irin waɗannan hanyoyin sadarwar kullum kara ɗaukaka suke yi da kuma sake samun sabon salo.
A ɓangaren abin da ya shafi Addinin Musulunci, waɗannan hanyoyin sadarwa na zamani kullum kara samun karɓuwa suke yi ga mabiya, da kuma jama’ar da suke son su san yadda ake yin addini ko kuma neman mafita a cikin abubuwan da suka shige musu duhu, ko kuma ga waɗanda ma ba su san addinin ba, suna son su san shi ko kuma me wannan addinin ya ke fada, ko domin kafa hujja da neman tozarta shi wannan addini, ko kuma neman diddigin me wane ya fada?
Mafi yawan mutanen mu da suke amfani da waɗannan sababbin hanyoyi suna amfani da su ta hanyar da ba ta dace ba, ko kuma suna amfani da su domin biyan buƙatunsu na yau da kullum a maimakon amfani da waɗannan hanyoyi domin bunƙasa addinin musulunci da yin da’awa mai kyau cikin hikima.
A karshen wannan taƙaitacciyar ƙasidar da zan gabatar (In Allah Ya yarda) zan yi magana ne a kan
- Mene ne Social Network?
- Tarihin Social Media
- Amfani da Social Media
- Musulunci da Fasahar Zamani
- Banbanci Tsakanin Social Media da Gidajen Yada Labarai
- Sawa Musulmai da Musulunci Ido a Duniya bayan harin 9/11
- Daukakar Addinin Musulunci bayan 9/11
- Dole Malamai su shiga social media
- Aikin Malamai a Socail Media
- Kiyaye harshe da alƙalami a intanet
- Shafukan da ya kamata malamai su bude ko mu’amala da su a Internet
Mene ne Social Network?
Social Media (shafuka ne ko manhajoji) hanya ce da ake yin amfani da ita a zamanance ta wurin yin mu’amala da jama’a a intanet domin fadin albarkacin baki ta hanyar yin rubutu, hadin gwiwa tsakanin mutane, musayar ra’ayi, da dai makamantansu.
Irin waɗannan shafuka (websites) ko manhaja (apps) na social media waɗansu su suna mayar da hankali ne wurin bayar da damar kirkiran dandali (forums), ko tura ƙananan sakwanni (microblogging), bunƙasa harkokin kasuwanci ko mu’amala tsakanin ɗaiɗaikun mutane (social networking), ajiyar kalmomi masu amfani (social bookmarking), matattarar shafukan intanet (social curation), da shafukan ajiyar bayanan gaggawa (wiki).
Waɗannan shafuka ana amfani da su ta hanyar ilmantarwa, nishadantarwa da faɗakarwa, tare faɗin abin da kake so a kuma lokacin da ka ke so.
Waɗannan shafukan za su iya samun rubutu zalla a cikinsu, ko kuma rubutun tare da liƙa musu hotuna masu motsi ko marasa motsi, ko kuma su ba jama’a damar ajiyar su hotunan a cikin ma’ajiyar wannan shafin.
Tarihin Social Media
Social Media kafin 1900
Idan muka ce za mu ɗauko magana a kan samuwar hanyar yin mu’amala da mutane wacce ita maƙasudin ko ginshiƙin social media to abu ne mai tsawo. Amma idan muka ce za mu danganta shi da yin mu’amala da jama’a ta hanya mai tsawo kuma ba tare da suna tare a wuri guda ba to za mu iya yin magana a lokacin fitowar telegraph wacce aka ƙirƙiro ta a shekarar 1792.
Telegraph a wancan lokacin ita ce ake amfani da ita wurin aikawa da sako a rubuce zuwa wani wuri mai nisa wanda saurin tafiyar tafi aike da abin hawa irin su Doki da makamantan su. Duk da cewar rubutun da ake aikawa da shi a wancan lokacin ba shi da yawa.
Bayyanar Wayar Tangaraho a shekarar 1890 da kuma bayyanar Rediyo a 1891 ya sake kawo sauyi mai yawa wurin yin mu’amala da mutane da suke wuri mai nisa. Duk da cewar har zuwa wannan lokaci da muke wannan magana ba a daina amfani da waɗannan Rediyo da Wayar Tangaraho ba amma kuma an sani sauya sauyen tsari, da kuma fasali a cikin fasahar su.
Social media a karni na 20
Kimiyyar fasaha da ƙere-ƙere ta canza abubuwa da yawa a cikin ƙarni na 20 canzawar da bata misaltuwa. Supercomputer ta farko an ƙirƙire ta ne a cikin shekarun 1940, daga wannan lokacin ne inginiyoyi suka bazama domin samun hanyoyin da za su iya sanya kwamfuta sama da daya ta iya ƙulla alaƙa tsakanin ta da ‘yar uwarta, wanda dalilin haka ne ya sa aka samu abin da muke kira a yanzu intanet.
Intanet a wancan lokacin irin su CompuServe an kirkiresu ne a wuraren 1960, kamar yadda imel na farko shi ma ya fito a wannan lokacin. A wuraren 1970s ƙulla alaƙa tsakanin kwamfutoci (networking) ya kara bunƙasa a wuraren 1979, kamfanin UseNet ya fara ba jama’a da su mu’amala da juna ta hanyar amfani da takardun su ta hanyar kwamfuta wato (virtual newsletter).
A wuraren shekarun 1980 kwamfutoci irin waɗanda muke amfani da su a gidaje da ma’aikatun mu suka fara yawaita a gidajen jama’a wanda daga wannan lokacin hanyoyin mu’amala da mutane suka ƙara ƙazancewa da yawa da kuma zama abin amfanin yau da kullum.
A wuraren 1988 aka fara yin amfani da intanet ayi magana na rubutu tsakanin jama’a wanda a yanzu muke cewa chating wanda ya ci gaba da tashe har zuwa cikin shekarar 1990s.
Shafin farko na intanet da aka fara kiran shi da social media shi ne shafin Six Degrees (sixdegrees.com) wanda aka ƙirƙire shi a 1997. Daga nan aka fara samun bayyanar shafuka a intanet waɗanda suke yin rubuce-rubuce a kan al’amuran yau da kullum.
Social Media a wannan lokacin
Bayan bayyanar shafukan rubuce-rubuce (blogging), daga wannan lokacin social media ta fara ƙarfi da bazuwa a shafukan intanet ba ji ba gani. Websites irinsu MySpace da LinkedIn a farkon shekarar 2000 suka fara shahara, kamar yadda website irinsu Photobucket da Flickr su kuma suka zama shafuka na farko da suke ba mutane damar daura hotuna. A shekarar 2005 shafin YouTube ya bayyana.
A 2006 shafin Facebook da Twitter suka bayyana ga mutanen duniya su yi amfani da shi. Wanda su waɗannan shafukan suka ci gaba da zama shafuka mafi shahara har zuwa wannan lokacin da muke ciki a yanzu.
Amfani da Social Media
A zuwa wannan lokaci kusan kullum ana samun ɗaruruwan shafukan sada zumunci wanda suke ɗauke da abubuwan ci gaba da kuma sake sabon salo na yadda jama’a za su samu sauƙi wurin yin mu’amala da jama’a.
Kamar yadda aka rubuta a shafukan ƙididdiga na brandwatch.com sun fadi cewar shafin Facebook shi ne shafin da ya fi kowane shafin zumunta yawan mabiya da kuma saka abubuwa a cikin sa wanda ya ke da mabiya sama da biliyan ɗaya da dubu ɗari bakwai (1.7 Billion). Amma ta wurin ziyarta da duba abubuwan da ke cikin intanet, shafin YouTube wanda ya ke ajiyar hotuna masu motsi ana kallon bidiyo a rana guda sama da biliyan ɗari da biyar (105 Billion).
Shafin internetlivestat.com sun ƙiyasta sama da mutume biliyan uku da rabi (3.7 Billion) suke amfani da intanet a duniya, wanda ya ke nuna cewar kusan rabin mutanen duniya ke nan. A Najeriya kuwa sama da mutane miliyan tamanin da shida (86 Million) suke amfani da intanet, kamar yadda sama da mutane miliyan sha bakwai (18 million) ke amfani da shafin sada zumunci na Facebook.
Idan muka duba ta ɓangaren amfani da ake yi da irin waɗannan shafuka sai mu ga ana amfani da su ta hanyar jawo ra’ayin jama’a zuwa ga abubuwan da mutane ba su san shi ba, ko manufofin waɗansu jama’a. Kamar yadda kuma ake amfani da irin waɗannan shafukan domin samun bayanai game da mutum da abubuwan da ya fi mayar da hankali a kansu.
Ana amfani da su wurin nuna ɗabi’u da al’adun mutane, aikace-aikacen jama’a da kungiyoyi, manufofin jama’a da yada addinan su, fadin ra’ayin da kare ra’ayi da dai makamantan su.
Saboda haka yaɗuwar kafofin sada zumunci a wannan lokaci sun yi karfin da bai kamata a ce an bar masu hankali da seta hankula wurin shiga domin a dama da su ba. Kamar yadda musulmai bai kamata a ce sun yi baya-baya ba wurin yin amfani da waɗannan shafuka domin yaɗawa da kuma kare martaba ta Addininsu da kuma mutuncin jama’ar su ba.
A baya, duniyar musulunci masu bincike sun mayar da hankalinsu wurin yiwuwar amfani da irin waɗannan kafafe na social media, waɗansu kuma suna duba amfanin shi da kuma illolinsa. Amma a yanzu tuni al’ummar musulmai suka fahimci cewar lallai yana da kyau su kasance a cikin wannan tafiyar musamman domin a wannan lokaci da ake ƙoƙarin yabawa Addinin Musulunci kashin da ba nashi ba.
Musulunci da Fasahar Zamani
A baya, abubuwan da suka shafi addinin musulunci ana samun su ne kawai a cikin littattafai, kaset-kaset na sauti ko na bidiyo, wanda ake ajiyar su a cikin gida, masallatai, ɗakin binciken ilimi, wanda musulmi ko wanda ba musulmi ba, ba zai iya samun su ba sai idan sun kusanci inda suke.
A yanzu haka za ka iya samun dukkan waɗannan tsarin ilimin na Alkur’ani, Hadisi, Sunnah, Sirah, Fiqhu da duk wani ilimi da mutum ya sani a shafukan intanet. Ana iya samun su da harshen Larabci, ko Turanci ko Hausa, Yarabanci, Inyamiranci da dai waɗansu yare da jama’a suka fi amfani da shi. Haka za ka samu irin waɗannan karatuttuka a rubuce, ko a cikin sauti, ko kuma a hotuna masu motsi da marasa motsi, dukkan su kuma a cikin intanet.
Haka kusan dukkan waɗannan abubuwan da muka lissafa za ka same su a cikin irin waɗancan shafukan na social media. Mu sani miliyoyin mutane a yanzu, musulmai da waɗanda ba musulmai suna mayar da hankalinsu a yanzu wurin yin amfani da irin waɗannan karatuttuka da muke sakawa domin sanin addinin musulunci da gaskiyar magana game da shi, ɗabi’u, halayya da kuma me jama’ar wannan addinin suke ciki.
Banbanci Tsakanin Social Media da Gidajen Yada Labarai
A zamanin baya kana bukatar kashe kudi sosai wurin daukar ɗawainiyar saka wani karatu ko sanarwa a gidajen Talabijin ko Rediyo, wanda irin waɗannan saƙwanni ba dole ya kai ga waɗanda ake so ba. Matsalar ɗaukewar wutar lantarki a yanzu ya isa mutum yayi asarar kuɗin da ya biya ko kuma jama’ar da yake bukatar su sami wannan sako. Neman isar da wannan sako ya takaita ga inda kake, misali wanda yake a Sakkwato idan ya bayar da sanarwa a gidan Talabijin na Sakkwato to ‘yan Sakkwato kawai zamu gani wanda ya ke wani gari ba zai gani ba.
Idan kuwa kana son wanda yake wani gari ya gani to ko dai ka aika da shi kowace jiha, ko kuma ka biya babban gidan Talabijin na Kasa domin ya saka, wanda shi ma magana ce ta kashe maƙudan kuɗaɗe.
Amma idan muka dawo ta bangaren shafukan intanet, su ba za mu hada su da gidajen Talabijin ko Rediyo ba domin matuƙar abin da aka saka na saƙo ko karatu ba a goge shi ba, to idan aka koma za a same shi.
Social media irin su facebook wanda muka ce yana da mabiya sama da (1.7b), cikin minti kaɗan idan ka saka saƙo ko karatu miliyoyin mutane ne za su samu, kuma za su gani a kowane lokaci kuma za su iya aikawa masoyansu wannan sako, masoyan masoyansu suma za su iya gani.
Haka ba dole sai a daidai wannan lokacin da ka saka wannan sakon za su gani ba, duk lokacin da mutum ya shiga cikin ɗakin sa zai ga sakon cewar wane ko shafi kaza sun saka abu kaza kuma idan ka taɓa wannan sakon zai sake bayyana ba tare da wata matsala ba.
Shi yasa ba yadda mutum zai iya daidaita muhimmancin waɗannan kafafen sada zumunci na zamani da kafafen yaɓa labarai na da da ake da su.
Sanyawa Musulmai da Musulunci Ido a Duniya bayan harin 9/11
Tun bayan da aka kai harin babbar cibiyar kasuwanci ta Duniya dake kasar Amurka, a 11/9/2001 musulmai da ke faɗin duniya suka shiga cikin wani mawuyacin hali musamman wadanda suke zaune a kasashen turai.
Sama da musulmai dubu 200 zuwa dubu 500 suka shiga cikin matsatsin bincike da kuma tsangwama a ƙasar Amurka, sama da musulmai dubu 18 aka mayar da su garuruwan su, musulmai dubu 15 wasu aka ɗaure su a gidan yari wasu kuma an tsare su domin tuhumar su.
An rage daukar ma’aikata Musulmai da kashi 10% a cikin Amurka gaba daya. Musulmi shi ne karshen wanda za a ɗauka aiki kuma shi ne farkon wanda za a fara sallama.
Duk takardar neman aikin da ta fara da sunan Muhammad ko Ahmad ba ta zuwa ko ina ba, kamar yadda sauran sunayen da ba su ba na musulmai suna iya tsallakewa. An kiyasta kashi 40% na Musulmai da suke garuruwan Brookly da New York da Chikago da Devon Ave sun rasa aikin su.
Kusan kashi 75% na musulman da suke kasar amurka zai wahala wani yace maka bai fuskanci tsangwama, cutar wa, wulaƙanta wa ko jifa da duka saboda wannan harin da aka kai.
Wannan harin da aka kai ya sanya kasar Amurka ta yaƙi ƙasar Iraƙi da Afganistan da kuma yaƙi da ta’addanci a fadin duniya baki daya.
Gidajen yada labarai da gidajen shirya fina-finan kasashen waje, gidajen Rediyo da Talabijin, Mujallu da Ƙasidu da shafuka a Intanet sun taimaka matuƙa wurin yaɗa furofaganda cewar addinin musulunci addinin ta’addanci ne da kuma addinin rashin son zaman lafiya.
Daukakar Addinin Musulunci bayan 9/11
Duk da irin waɗancan abubuwa da suka faru da kuma takura da musulmai suka yi a cikin wannan ƙasar ta Amurka, bai hana wannan addinin ƙara ɗaukaka ba, domin kamar yadda aka rubuta a cikin wata ƙasida mai take “A Wave of Conversion to Islam in the U.S. Following September 11” cewa sama da mutane dubu 34 ‘yan ƙasar Amurka ne suka karɓi Addinin Musulunci bayan da aka kai harin 9/11.
Ƙoƙarin da Musulman ƙasar Amurka suka yi da kuma juriya da canza salon mu’amala da fito da haƙiƙanin karantarwar Addinin Musulunci da rubuce-rubuce a shafukan sada zumunci irin na social media sun taimaka matuka wurin kara fahimtar addinin musulunci.
Addinin musulunci a yanzu shi ne addini na uku da ya fi yawa a kasar Amurka, bayan kiristanci da addinin buda, kuma musulunci shi ne addinin da ya fi karbuwa a cikin wannan kasa a yanzu. A yanzu akwai sama da masallatai na salloli biyar sama da dubu biyu da dari biyar.
Kafin lokacin da yawan turawan yamma babu abin da ya shafe su da addinin, da yawa daga cikinsu mutane ne waɗanda ko imani da cewar akwai wanda ya hallici duniya ba su yi ba, ballantana su yi imani da kiristanci ko kuma addinin musulunci.
Irin rubuce-rubucen da suka cikin Intanet dangane da karantarwa ta Addinin musulunci ya taimaka wurin kara fahimtar musulunci da kuma me addinin yake karantarwa.
Dole Malamai su shiga social media
Kasancewar malamai suna suka fi kowa hankali da sanin abin da ya dace da al’umma da zamaninsu ya sanya wajibi ne kowane malami mai da’awa ya kasance a kalla yana da shafi a cikin wadannan shahararren gidaje a intanet domin isar da sakon Allah madaukakin sarki.
Kasancewar wadannan shafukan suna da yawa, kuma akwai abubuwan da ya kamata malamai su sani na shirme da shiriri ta da batanci ga addinai, da rashin girmama mutane, da rashin kamun kai, da rashin boye tsaraici da fito da alfahasha da abin ki.
Kasancewar daya daga cikin wadannan abubuwan da muka lissafo ya sanya wajibi ne malamai su shiga cikin irin wannan shafuka domin yin wa’azi da kuma gyara ta hanyar da ya dace.
Matsalar da muke fama da ita a irin waɗannan sababbin al’amura shi ne malami ya yanke wani hukunci cikin abin da bashi da cikakkiyar masaniya akai, musamman lokacin da yake son yayi gyara akan abu alhali bai san wannan abin ba ko kuma bai ma taba yin mu’amala da shi ba.
Aikin Malamai a Socail Media
‘Yancin yin magana:- Daya daga cikin cikin abin da ya fi shahara a cikin irin wadannan shafuka shi ne yar da jama’a suka cewar kowa na da ‘yancin fadin abin da ya ga dama ko da kuma zai ci karo da cin mutunci ko batanci ga wani ko kuma tozarta addinin wani.
A nan aikin da malamai za su yi shi ne su fadawa mabiyansu yin magana cikin abin da ya kasance maslaha ga al’umma da kuma fada musu cewar mutum musulmi ba shi da ‘yancin fadin komai da ya ga dama, kuma babu wani dalilin da zai sa saboda ka sada da wani a ra’ayi kace zaka fadi maganar da kaga dama. Musulunci shi ya zo da kame harshe mutukar mutum ya san ba alkairi zai fada ba.
Gyaran Tarbiyya:- Samari da yawa da ‘yan mata suna shiga cikin wadannan shafukan domin holewa da kuma samun sababbin abonkai da sanin abubuwan rayuwa. Daga cikin abin da ya fi damun mutane da social media shi ne rashin tarbiyya da ake yadawa a ciki, wanda kuma zai wahala ka samu irin wadannan yaran basu da alaka da wani shafi na wani sanannen malamin addini, ko kuma group na mutanen kirki wadanda suke fadakarwa da kuma yin nasiha ga irin wadannan dabi’u marasa kyau.
Batanci Ga Addini:- Wannan daya ne daga cikin matsalar da ake fama da ita cikin intanet da kuma social media. Domin idan ba wani wuri da ya kamata malamai su rika yin saurin yin magana da Musulmai irin mayar da martani a lokacin da aka yi batanci ga Addinin Musulunci ko kuma Ma’aiki SAW.
Idan muka duba yawan mutanen da suke cikin intanet musamman social media za muga cewar kusan mutane biliyan uku ne (3billion), to me kake tsammani zai faro a lokacin da wanda ba shi da ra’ayin addininka ya tashi yin wata magana ta batanci ga addinin?
A wannan wurin ya ke da muhimmanci malamai su shigo domin baiwa wannan addinin kariya cikin hikima da kuma bayar da gamsassun hujjoji domin kariyar wannan addinin. Domin da za ace abar wanda bashi da ilimi yayi magana a cikin irin wannan al’amari to zaka samu cewar abubuwan kara bace suke yi ba wai gyaruwa ba.
Idan muka duba irin yadda malamai turawa irin na kasashen waje musamman irin su, Zakir Nail, Yusuf Estes, Khalid Yasin, Muhammad Auwal zamu ga cewar duk lokacin da wani ya fito yayi batanci ga addinin musulunci su kuma suna shiga kafefen intanet domin su jawo hankalin mabiyansu da kasa su mayar da wani martani domin zai iya yuwuwa sun yi haka ne domin takalar musulmai da musulunci.
Rashin Girmama Mutane:- Idan kana bibiyan rubutu da ake yi a irin wadannan shafuka na sada zumunci sai ka samu mutanen da suke kiran kansu masu hankali sai ka samu suna kuma yin abubuwa na rashin girmama mutane ko kuma ra’ayin mutane.
Shafin sada zumunci cike yake da sabanin ra’ayi, duk inda mutum ya ke da kokarin yin bayani gamsasshe dole sai wani ya ji an saba mishi ta wani wuri, shi yasa zaka samu rashin girmama ra’ayin jama’a da kuma yin magana ta adalci ga wani mutum da ya kawo sabanin ra’ayi.
A nan malamai za su iya kawo sauyi wurin koyawa mabiyansu yadda ake yin magana da ta sabawa ra’ayi, da kuma kore zage-zage da aibace-aibace da ya cika wannan gidaje.
Rashin Boye Tsaraici:- Idan aka yi magana a kan tsaraici to ba a iya cewa komai a intanet ko social media, duk da cewar kamfanonin da suke da wadannan shafuka suna kokari matuka wurin tsaftace shafukansu daga irin wadannan hotuna na batsa ko tsiraici.
A nan malamai za su iya shigowa domin kawo sauyi ta hanyoyi da dama, kamar yin rubuce-rubuce da wa’azoji a shafukansu na hatsarin irin wadannan abubuwa da ba su dace ba.
Kiyaye harshe da alkalami a intanet
Yana da kyau malamai su sani cewar babu abin da ya fi intanet ko social media saurin yada abu a duniya, wannan ya ke nuna mana cewar ya zama wajibi malamai su san me zasu fada a lokacin da suke gudanar da muhadarorinsu ko wa’azi ko kuma wani rubutu wanda ba zai dauki wata fuska ko ma’ana ba.
Babu wanda zai fada malami mai ya dace ya fada, amma kuma kamar yadda ka san cewar magana zarar bunu ce, to haka rubutu a intanet ya ke, duk abin da ka rubuta miliyoyin mutane za su iya ganin cikin dan kankanlin lokaci, kuma nan take wadansu za su fara yada shi ba tare da ka basu umarni ba.
A wannan lokacin da musulmai suke neman hanyar da zasu gamsar da jama’ar duniya kyawawan dabi’un musulunci, yana da kyau su sani dukkan wani rubutu ko karatu da za su saka a cikin shafukansu to ya kasance bai bada wata kofa da zai kara dakushe karfin addini ba.
Malamai su sani cewar yaki dan zambo ne, duniya ta zare takobin yaki da musulunci da musulmai, saboda haka a wannan lokacin yana da kyau a kiyaye saurin yanke hukunci a cikin duk wani al’amari da aka ga wani ya yi dangane da batanci ko kuma soke wani ra’ayi ko hukunci na addinin musulunci da gaggawa.
Malaman da suka fahimci zamanin su sun san sau tari wani abu da ake yi a cikin social media ana yinsa ne domin a tunzura musulmi, saboda haka saurin yanke hukunci ko kuma yin gaggawar fadin magana zai iya kaiwa ga sake fito da wata matsalar ko kuma wata barna.
Lokacin da turawan faransa suke kokarin yin batanci ga fiayyen hallita Annabi Muhammad SAW, ta wurin zana shi ta mummunan hotuna, da shirya fina-finai na yara domin cimma wannan manufa ta su.
Daya daga cikin manyan malamai masu yin da’awa kuma limamin juma’a Muhammad Auwal ya ce ya kira sauran malamai irin su Yusuf Estes, Khalid Yasin domin su yi rubutu a kan kyawawan dabi’un Annabi Muhammad SWA. A wannan satin sai da suka sami karuwar daruruwan musulmai wadanda ba su taba sanin musulunci ba.
Duk lokacin da wani ya yi batanci ga addinin musulunci ko da masu da’awar musulunci ne wadadna suke kai hari domin kashe mutane babu gaira babu dalili, ko kuma ke zargin wani malami da ta’addanci gidajen yada labarai suna kokarin yadawa, wani lokacin ma sai ka ji kamar babu wani abin da wadannan gidajen jaridu suke yi sai hakan.
A gefe guda kuma, wadanda ba su da ilimi ko sani game da wannan addinin ko kuma abin da wannan malami ya ke yi, suna shiga shafukan intanet su yi ta bincike game da wannan al’amari wanda ya ke yanzu ra’ayin su suke koma addinin musulunci.
Shafukan da ya kamata malamai su kasance a ciki
Kasancewar su wadannan shafuka suna da yawa wanda sanin adadinsu sai Allah, kuma ba kowanne ba ne yake da muhimmanci kuma ba kowanne ba ne jama’a suka yin mu’amala da shi ba, ya sanya na zabo abubuwa guda bakwai da ya kasance malamai su shiga cikinsu domin su taimaka wurin isar da sakon Allah.
Website/Blog
Mallakar shafin malami na shi na karankanshi ya fi komai muhimmanci domin a nan ne za a iya samun rubutunshi ko wa’azozin shi, ko karatukansa. Shi mallakar wannan shafin ya na matakai masu dama, tun gaba mallakar suna, dakin da zaka adana bayanai da kayanka da kuma wanda zai kirkiri wannan shafin da kuma lura da abin da za a saka a cikinsa.
Shafin facebook shine shafin da ya fi kowane yawan mabiya,wanda yake da mabiya kimanin,bilyon daya da dubu dari takwas,a najeriya yana mabiya kimani mutane miliyan goma sha takwas,wanda yana da kyau ace kowane malami yana da account a shafin facebook kuma yana da page din zuba bayanai game da addini (fans page).
Shafin twitter shima shafine da yakamata ace malamai su mai da hankali akanshi, wanda shine farkon microbloging web site wanda yake ba mutane dama suyi rubutun wasika da bata wuce harufa dari da sit
YouTube
Youtube shafi ne wanda yake ba mutum dama ya daura video komin yawanshi komin nawinshi, wanda ake shiganshi sama da bilyon hudu a rana,
Sound Cloud
Sond cloud shafi ne wanda yake ba mutum dama ya dora ko wane irin karatu a cikin sauti
Linkedin shafi ne da yake bamawa mutum dama ya rubuta game da shi,tarihinshi,inda yayi karatu,matsayinshi a fannonin rayuwa.
Wikipedia
Wikipidia shafi ne da ya shahara wurin baiwa mutane damar warware mas’aloli akan ilimi, mas’alolin da suka shafi tarihin wani.
Rufewa
Kamar yadda muka ji a yanzu yana da kyau malamai su fahimci cewar Social media yana da matukar muhimmanci gare mu, domin amfani da shi wurin wayar da kan alumma game da abin shafi addini na karatuttuka, da kara bunkasa harkokin addini, tare da fadakarwa da nasihohi ga alummar Musulmi
Menene internet
Menene internet